Uncategorized

A karon farko da mahaifiyar murja Ibrahim tayi martani akan yadda mutane suke….

Akaron farko da mahaifiyar murja Ibrahim tayi martani akan yadda mutane suke….

Bayan kamun da hukumar hisbah tayi wa fitacciyar yar Tiktok Murjanatu Ibrahim kunya wanda a kafar tiktok ke amfani da sunan yagamen yanzu dai tana asibitin dawanau inda take karkashin kulawar Hukumar hisbah har nan da wasu yan watani kafin a koma kotu.

Wani labari ya fito da ke nuna za’a yiwa murja kunya allurar mahaukata taƙi amincewa da ayi mata ita, shine fa mahaifiyar take mayar da magana akan wannan aika aikar da ake son yiwa diyar kamar yadda majiyarmu ta samu wani faifan sautin murya da dokin karfe tv na mahaiyarta ta bayyana.

Sunana haditul kubura, nice nan mahaifiyar Murjanatu Ibrahim kunya , ance an kaita asibiti ana mata magani naji na dauka na yarda, asibitin nasarawa, sai jiya wani abu ya taso anka kirani inyi maza maza inzo tana kuka da ranta za’a kashe min ita a takaice a guje naje asibitin dawanau na tarar da ita kuka, ni ina kuka munka rungumi juna.

“Ni kuma nace bana buƙatar ayiwa ƴarta allurar mahaukata don ba mahaukaciya bace, sai nake tambaya wannan ba asibitin mahaukata bace anka ce eh nace to miye dalilin kawo min ƴarta nan ayi mata allurar mahaukata.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button